fidelitybank

Tinubu ya gargaɗi ƴan kasuwa masu ɓoye kayan abinci

Date:

Gwamnatin tarayya ta gargaɗi ‘yan kasuwar da ke da ɗabi’ar ɓoye kayan abinci a daidai lokacin da talakawan ƙasar ke cikin matsin rayuwa.

Ministan yaɗa labaran ƙasar Muhammad Idris ne ya bayyana haka jim-kaɗan bayan taron gaggawa kan halin matsin rayuwa da tsadar abinci da ‘yan ƙasar ke ciki.

Ministan ya ce gwamnati a nata ɓangare za ta fito da metri ton 42,000 na abinci daga rumbunan ma’aikatar harkokin noma.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke cikin matsin tattalin arziki da tsadar rayuwa da ake fuskanta a cikin makonnin baya-bayan nan.

”Ma’aikatar harkokin noma na da masara da gero da nau’in gari a rumbunan ajiyarta da ke sassan ƙasar daban-daban domin raba wa ‘yan ƙasar nan ba da jimawa ba”, in ji ministan.

Ya ƙara da cewa gwamnati ta ji labarin cewa masu kamfanonin sarrafa shinkafa faɗin ƙasar na da tarin shinkafar da suka taskance, don haka gwamnati ta yi magan da su sun kuma amnce za su fito da metric ton 60,000, don a sayar wa ‘yan ƙasar.

Ministan ya ce idan ta kama ma ƙasar za ta ya shigo da abinci daga ƙasashen wajen do magance matsalar tsadar abincin a faɗin ƙasar.

”Nan gaba kaɗan za a yi haka idan ta kama a yi”, in ji Muhammad Idris.

Ministan ya kuma gargaɗi masu ɓoye kayan abinci da su buɗe shagunansu domin mutane su samu damar saya.

”Ba abu ba ne na alkairi ana cikin wannan matsatsi, kai kuma ka je ka ɓoye abinci don wata manufa taka da daban, don haka gwamnati ke kira ga irin waɗanan ‘yan kasuwa da su fito da waɗanan kayayyaki domin sauƙaƙa wa ‘yan ƙasa”, in ji ministan.

Yana me cewa duk ɗan kasuwar da ya ki bin wanan umarni to gwamnati ta san su ta kuma san matakin da za ta ɗauka a kansu.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp