fidelitybank

Tinubu ya gana da ‘yan kasuwa domin shawo baki zaren

Date:

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wata ganawa da manyan ‘yankasuwa masu zaman kansu da wasu gwamnonin jihohin ƙasar, inda suka tattauna halin da tattalin arzikin kasar ke ciki da kuma tsadar rayuwar da ‘yanƙasar ke fuskanta.

Taron ya kuma tattauna kan yadda darajar kuɗin kasar, Naira ke faɗuwa yayin da darajar dalar Amurka ke ƙara tashi, a yayin ganawar ta ranar Lahadi.

Baya ga batun tattalin arziki taron ya kuma tattauna kan batutuwan da suka shafi wadata ƙasar da abinci da kuma na tsaro.

Shugaba Tinubu ya jaddada cewa “kamar yadda na sha faɗa al’ummar kasar nan su ne kaɗai mu ke da su, kuma muke son kyautatawa, mun damu matuƙa da halin da suke ciki”

Cikin waɗanda suka halarci taron a fadar gwamnatin ƙasar da ke Abuja, sun haɗa da attajirin ɗankasuwan nan, Alhaji Aliko Dangote.

“Mun tattauna kan batun samar da ayyukan yi da wasu batutuwa da dama… abin alfaharin shi ne Najeriya ƙasa ce mai albarka, kuma mu na da kyakkayawan fata kan za mu iya sauya tattalin arzikinmu kuma za mu tabbatar da hakan.” In ji Dangote.

Taron na zuwa ne a daidai lokacin da ƙungiyar ƙwadago ta NLC ke shirye-shiryen yin zanga-zanga kan tsadar rayuwa.

Miliyoyin ƴan ƙasar ne ke rayuwa cikin ƙangin talauci da yunwa, lamarin da ake alaƙantawa da cire tallafin mai da kuma sauran gyaran fuskar da shugaban ƙasar ya yi tun bayan hawansa mulki.

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp