A daren ranar Alhamis din da ta gabata ne tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu, ya ziyarci jihar Kano, domin neman goyon bayan wakilan da zasu fafata a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC.
Tinubu ya gana da jiga-jigan jam’iyyar APC da wakilai a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati, Kano.
Kamfanin dillancin labarai na ƙasa (NAN) ya ruwaito cewa, Tinubu na daya daga cikin masu neman tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023.
Ziyarar tasa ta zo ne kwanaki kadan bayan wasu masu neman takarar shugaban kasa biyu mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amechi sun ziyarci jihar domin suma su samu goyon bayan wakilan.