fidelitybank

Tinubu ya gana da gwamnoni kan tsadar rayuwa da al’umma ke ciki

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya gana da gwamnonin ƙasar a zauren majalisar dokoki da ke Abuja.

Taron wanda aka fara da misalin karfe 11:30 na safe, ya samu halartar mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima da ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike; da Sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun.

Taron dai bai rasa nasaba da damuwar da ake nunawa a fadin kasar dangane da tsadar kayan abinci da rashin tsaro da sauran batutuwan da suka shafi tattalin arziki.

Taron dai ya biyo bayan taron Majalisar Tattalin Arzikin Kasa (NEC) na wata-wata, wanda mataimakin shugaban kasa Shettima ya jagoranta.

Bayan koke-koke da al’ummar kasar suka yi kan tabarbarewar tsaro da tabarbarewar tattalin arziki, shugaban kasar ya umarci ma’aikatar noma da samar da abinci ta saki kimanin tan dubu arba’in da biyu na masara da gero da sauran kayayyakin masarufi a cikin tsare-tsare don magance hauhawar farashin kayan abinci a kasar.

Shugaban ya kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da zuba ido kan ƙalubalen tattalin arziƙi da tsaro da Najeriya ke fuskanta.

Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu ta yi ciki har da cire tallafin man fetur ya zama dole, inda ta kara da cewa wadannan matakan za su haifar da riba nan ba da jimawa ba.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp