fidelitybank

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Date:

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta karɓi Najeriya ne lokacin da tattalin arzikin ƙasar ya kusa durkushewa.

Wike ya bayyana haka ne a cikin shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels ranar Juma’a.

Ya yi watsi da iƙirarin cewa gwamnatin Tinubu ta lalata ɓangaren tattalin arzikin Najeriya.

“Ya gaji tattalin arzikin da ya samu tawaya, wanda kuma ya kusa durkushewa,” in ji Wike.

Ministan na Abuja ya ce Allah ne ya ceci Najeriya da ya kawo shugaba Tinubu saboda kaɗan ya rage a binne ƙasar.

“Najeriya ta yi sa’a da zuwan Tinubu saboda ƙiris ya rage a binne ta. Mun yi farin ciki Tinubu ya zo ya ce hakan ba zai faru ba, ‘Ba zan ba ri ku shiga matsala ba”.

Ya ce cire tallafin man fetur da aka yi yana da alfanu sosai saboda zai samar wa jihohi ƙarin kuɗaɗen kashewa, ba kamar yadda wasu ke cewa tsarin ba mai kyau bane duk da cewa an fuskanci matsaloli.

Wike ya ce ya yi wuri a yi wa gwamnatin Tinubu alkalanci a ƙasa da shekara biyu kan mulki, inda ya yi kira da a ci gaba da marawa gwamnatin baya.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp