fidelitybank

Tinubu ya fi kama masu zanga-zanga maimakon kama ‘yan ta’adda – Atiku

Date:

Jagoran adawa, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin ƙasar da mayar da hankali kan wasu abubuwa da ya kira marasa muhimmanci tare da yin watsi da matsar tsaro da ƙasar ke fama da ita.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, tsohon ɗan takarar shugaba ƙasar na jam’iyyar PDP ya yi Allah wadai da harin da mayaƙan Boko Haram suka kai jihar Yobe, da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Ya kuma yi tsokaci kan yawan tashe-tashen hankula da ke ci gaba da faruwa a jihohin Katsina da Sokoto da sauran sassan Arewa.

Atiku ya zargi gwamnati da cewa ta fi damuwa da kama masu zanga-zanga, maimakon magance matsalar rashin tsaro.

“Duk da mummunan zubar da jini da aka yi a Yobe, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama, da kuma ɓarnar da aka yi a ƙauyuka da dama a Katsina da Sakoto, da sauran garuruwan da ke yankin arewa maso yamma da arewa ta tsakiya, da dukkan alamu gwamnati ta fi mayar da hankali kan ayyukanta da sauran abubuwa da ba zu da muhimmanci.” in ji Atiku.

Atiku ya kuma yi nuni da tashe-tashen hankulan da ‘yan Boko Haram ke haifarwa da rigingimun siyasa a kudu.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp