fidelitybank

Tinubu ya damu da ‘yan kabilar Inyamurai – Kalu

Date:

Benjamin Kalu, mataimakin kakakin majalisar wakilai, ya ce Shugaban kasa Bola Tinubu ne kadai shugaban kasar da ya tuna da kabilar Igbo tun bayan yakin basasa.

Kalu ya yi wannan magana ne a ranar Asabar yayin wani shirin tallafawa al’umma da Chris Nkwonta, dan majalisa mai wakiltar mazabar Ukwa East/Ukwa West, ya shirya.

An gudanar da taron a Ndoki, cikin karamar hukumar Ukwa East na jihar, inda aka ce sama da mutane 3,000 daga jam’iyyun siyasa daban-daban suka sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Kalu ya ce wannan sauya shekar alama ce ta godiyar jama’a ga Tinubu, wanda ya dukufa kan ci gaban al’ummar Ndigbo, musamman ta hanyar kafa hukumar raya yankin Kudu maso Gabas (SEDC).

“Shugaban kasa ya yi kokari wajen taimakon Ndigbo. Har yanzu yana kokari ga Ndigbo. Shi ne kadai mutum da ya tuna da Ndigbo bayan shekara 54 da aka yi alkawarin sake gini, sulhu da gyara ga Ndigbo,” in ji Kalu.

Kalu ya ce sake gini, gyara da sake hadewar yankin Kudu maso Gabas ya fara ne da kafuwar SEDC.

“Ya zo da adalci da gaskiya. Shi jagora ne da ke da yakinin ci gaba. Ya rattaba hannu kan dokar SEDC don a gyara barnar da yakin basasa ya haifar,” in ji mataimakin kakakin majalisar.

“A matsayinsa na jagoran jam’iyyarmu, ya umarce mu da mu karfafa guiwar jama’a a matakin kasa da kuma kusantar da su ga manufofin ci gaban da yake kawo wa ƙasar Igbo.

“Don daukar wannan matakin shiga APC, za ku samu alheri. APC ta kusantar da kanta da mutane. A madadin jam’iyyarmu, muna maraba da ku. Mun san su waye ku da abin da za ku iya yi.”

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp