fidelitybank

Tinubu ya damu da ‘yan kabilar Inyamurai – Kalu

Date:

Benjamin Kalu, mataimakin kakakin majalisar wakilai, ya ce Shugaban kasa Bola Tinubu ne kadai shugaban kasar da ya tuna da kabilar Igbo tun bayan yakin basasa.

Kalu ya yi wannan magana ne a ranar Asabar yayin wani shirin tallafawa al’umma da Chris Nkwonta, dan majalisa mai wakiltar mazabar Ukwa East/Ukwa West, ya shirya.

An gudanar da taron a Ndoki, cikin karamar hukumar Ukwa East na jihar, inda aka ce sama da mutane 3,000 daga jam’iyyun siyasa daban-daban suka sauya sheka zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Kalu ya ce wannan sauya shekar alama ce ta godiyar jama’a ga Tinubu, wanda ya dukufa kan ci gaban al’ummar Ndigbo, musamman ta hanyar kafa hukumar raya yankin Kudu maso Gabas (SEDC).

“Shugaban kasa ya yi kokari wajen taimakon Ndigbo. Har yanzu yana kokari ga Ndigbo. Shi ne kadai mutum da ya tuna da Ndigbo bayan shekara 54 da aka yi alkawarin sake gini, sulhu da gyara ga Ndigbo,” in ji Kalu.

Kalu ya ce sake gini, gyara da sake hadewar yankin Kudu maso Gabas ya fara ne da kafuwar SEDC.

“Ya zo da adalci da gaskiya. Shi jagora ne da ke da yakinin ci gaba. Ya rattaba hannu kan dokar SEDC don a gyara barnar da yakin basasa ya haifar,” in ji mataimakin kakakin majalisar.

“A matsayinsa na jagoran jam’iyyarmu, ya umarce mu da mu karfafa guiwar jama’a a matakin kasa da kuma kusantar da su ga manufofin ci gaban da yake kawo wa ƙasar Igbo.

“Don daukar wannan matakin shiga APC, za ku samu alheri. APC ta kusantar da kanta da mutane. A madadin jam’iyyarmu, muna maraba da ku. Mun san su waye ku da abin da za ku iya yi.”

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp