fidelitybank

Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 1.1 don samarwa mutane miliyan 5 wutar lantarki

Date:

Najeriya ta karɓo rancen dala biliyan 1.1 daga bankin raya Afirka (AfDB) don samar da wutar lantarki ga mutane miliyan 5 daga yanzu zuwa ƙarshen shekarar 2026.

A cewar Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa shawara na musamman, Shugaba Bola Tinubu ya bayyana hakan a cikin jawabin da Adebayo Adelabu, ministan wutar lantarki, ya gabatar, a taron da aka kammala na kwanaki biyu na inganta ɓangaren makamashi na Afirka a Dar es. Salaam, babban birnin ƙasar Tanzania.

Tinubu ya kuma bayyana cewa za a yi amfani da dala miliyan 200 na AfDB domin samar da wutar lantarki ga mutane 500,000 a ƙarshen shekarar 2025.

“Wannan babban buri ne, amma za mu iya cimma shi tare,” in ji Tinubu.

“A matsayina na shugaban Najeriya, na himmatu wajen ba aiwatar da aikin samar da makamashi, kuma mun ba da babban fifiko.”

Ya ƙara da cewa “Kamar yadda muka sani, Afirka na da wadatar albarkatun makamashi, amma har yanzu miliyoyin ƴan nahiyar mu ba sa samun ingantaccen makamashi mai araha.”

Shugaba Tinubu kuma jinjinawa Ajay Banga, shugaban bankin duniya, da Akinwunmi Adesina na AfDB saboda hangen nesan su na kawo sauyi, wanda ya ce “zai haskaka da kuma karfafa Afirka.”

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp