Shugaban kasa Bola Tinubu ya nemi majalisar dokokin ƙasar ta amince masa karɓo bashin naira tiriliyan 1.767 daga ƙasashen waje domin cike gurbin kasafin kuɗi na 2024.
Tinubu ya nemi hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, da kuma Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas, wadda kuma suka karanta ta a yau Talata.
Kuɗin da majalisar zartarwa ta amince da su, za a yi amfani da tiriliyan 9.7 daga ciki wajen cike giɓin kasafin na 2024, idan majalisar ta amince.
Haka nan, Tinubu ya miƙa daftarin kasafin kuɗi na shekarar 2025 zuwa 2027 ga ‘yanmajalisar, da kuma ƙudirin kafa dokar shirin kyautata rayuwar jama’a domin mayar da rajistar ‘yan ƙasa a matsayin wadda za a dinga amfani da ita wajen kyautata rayuwar ‘yan Najeriya.
A makon da ya wuce ne gwamnatin ta ce za ta ciyo bashin ƙasashen waje da ya kai dala biliyan biyu domin yin amfani da su a ɓangarori daban-daban.