fidelitybank

Tinubu ya bayyana kadarorinsa – Hukumar Da’ar Ma’aikata

Date:

Hukumar kula da Da’ar Ma’aikata ta Najeriya ta ce dole ne zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima da gwamnonin ƙasar 28 da ke jiran rantsuwa su bayyana kadarorinsu kafin ranar 29 ga watan Mayu.

Haka kuma hukumar ta ce su ma zaɓaɓɓun ‘yan majalisun wakilai da na dattawa za su bayyana nasu kadarorin kafin ranar 5 ga watan Yuni lokacin da za a rantsar da su.

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito mai magana da yawun hukumar Mrs Veronica Kato, na cewa bayyana kadarorin, wani ɓangare ne na shirye-shiryen shan ratsuwar kama aiki ga zaɓaɓɓun shugabannin kamar yadda dokar ƙasar ta tanadar.

Mrs Kato, ta ce da yawa daga cikin zaɓaɓɓun sun fara karɓar fom ɗin bayyana kadarorin a rassan ofisoshin hukumar da ke faɗin jihohin ƙasar, kuma ana sa ran za su mayar da fom ɗin zuwa ofisoshin tare da bayyana kadarorin kafin ranar rantsar da su.

Kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanadi cewa masu riƙe da muƙaman siyasa su bayyana kadarorin da suka mallaka a lokacin da za su kama aiki da kuma a lokacin da suka kammala wa’adin mulkinsu.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp