fidelitybank

Tinubu ya bayar da umarnin a gaggauta bincike bayan an jefa bam a Kaduna

Date:

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin gudanar da bincike cikin gaggawa kan harin bam da sojojin Najeriya suka kai a Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna a ranar Lahadin da ta gabata, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale, ya fitar ranar Talata, shugaban ya jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa da kuma gwamnatin jihar Kaduna.

“Shugaba Bola Tinubu ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da jama’ar jihar da kuma gwamnatin jihar Kaduna kan tashin bam a wani kauye da ke Tundun Biri a karamar hukumar Igabi a jihar.

“Shugaba Tinubu ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, mai tayar da hankali, kuma mai raɗaɗi, yana mai nuna fushi da baƙin ciki game da mummunar asarar rayukan da aka yi a Najeriya.

“Shugaban kasa ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da yin kira da a kwantar da hankula yayin da hukumomi suka yi nazari sosai kan lamarin.

Sanarwar ta kara da cewa “Shugaban ya kuma ba da umarnin kulawar gaggawa ga wadanda abin ya shafa yayin da yake addu’ar samun lafiya ga rayukan wadanda suka mutu.”

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya tabbatar da cewa rundunar Sojin ta dauki alhakin kai harin ta sama wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama a ranar Lahadi.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp