fidelitybank

Tinubu ya bayar da umarni a duba rahoton yuwar rage ma’aikatu tare da haɗe wasu

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya ba da umarnin aiwatar da cikakken rahoton Oronsaye wanda tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kafa tun a 2011, a kokarin gwamnati na rage yawan kashe kudaden gudanarwa.

An dai kafa kwamitin ne a lokacin sake fasalin tsarin mulki da kwamitoci da hukumomin gwamnatin tarayya karkashin shugabancin tsohon shugaban ma’aikata na Najeriya, Stephen Osagiede Oronsaye.

Kwamitin ya gabatar da rahoto mai shafuka 800 a ranar 16 ga Afrilu, 2012, inda ya bankado yadda ake gudanar da gasa a tsakanin hukumomi da dama, wanda ba wai kawai ya haifar da rashin kwanciyar haknali a tsakanin hukumomin gwamnati ba, har ma ya haifar da almubazzaranci.

Rahoton ya ba da shawarar dakatar da tallafin da gwamnati ke bai wa wasu hukumomi da majalisu wajen bayar da kuɗi don gudanar da manyan ayyuka.

Rahoton na Oronsaye ya tabbatar da cewa akwai ma’aikatun gwamnatin tarayya 541 da kwamitoci da hukumomi (na doka da na shari’a), inda ya bayar da shawarar cewa a mayar da 263 daga cikin ma’aikatun zuwa 161, yayin da rahoton ya ce a soke hukumomi 38 sannan a hade guda 52.

Kwamitin ya kuma ba da shawarar cewa 14 daga cikin hukumomi su koma sassan ma’aikatu.

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris, da yake jawabi ga manema labarai a fadar shugaban ƙasa a ranar Litinin a Aso Rock, Abuja, ya ce “a cikin wani gagarumin yunkuri a yau, gwamnatin shugaban Tinubu ta dauki matakin aiwatar da rahoton da ake kira Oronsaye Report don amfanin Najeriya”

“Yanzu, abin da hakan ke nufi shi ne, an soke wasu hukumomi da kwamitoci, da wasu sassa a zahiri. Wasu kuma an gyara su, kuma an yi musu alama yayin da wasu kuma an rage su. Wasu kuma, ba shakka, an dauke su daga wasu ma’aikatun zuwa wasu inda gwamnati ke ganin za su yi aiki sosai.”

Da take tsokaci kan wannan lamari, mai bai wa shugaban kasa shawara ta musamman kan harkokin siyasa Hadiza Bala Usman, ta ce hakan ya yi daidai da buƙatar rage yawan kudaden gudanar da harkokin mulki da kuma daidaita yadda ake tafiyar da harkokin gwamnati.

Ta kara da cewa an kafa tawaga don aiwatar da rahoton cikin makonni 12.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp