Gwamnatin tarayya ta ayyana Laraba, 1 ga watan Mayun 2024, a matsayin hutu, domin bikin ranar ma’aikata na wannan shekara.
Ministan harkokin cikin gida na Najeriya, Olubunmi Tunji-Ojo, shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa yau Talata.
“Gwamnatin tarayya ta ayyana Laraba, 1 ga watan Mayu, a matsayin hutu domin bikin ranar ma’aikata,” a cewar sakatariyar dindindin na ma’aikatar a cikin wata sanarwa.
Ta ambato ministan na sake nanata bukatar ganin ma’aikata sun jajirce da yin aiki yadda ya kamata a dukkan matakai.