fidelitybank

Tinubu ya amince da kafa asusun more rayuwa a jihohi 36

Date:

Shugaban ƙasa Bora Ahemd Tinubu, ya amince da kafa asusun gina ababen more rayuwa a jihohi 36, a wani mataki na rage wa yan kasa radadin cire tarafın man fetur.

Shugaban ya amince da matakin ne a lokacin taron wata wata na kamitin kula da asusun raba kudin, shiga na gwamnatin kasar (FAAC) da aka gudanar ranar Alhamis a Abuja.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar Dele Alake ya fitar, ya ce sabon asusun zai taimaka wa jihohin kasar wajen zuba jari a bangarorin sufuri da harkokin noma da gina tituna da kasuwanni da kiwon dabbobi da bangaren lafiya da ilimi musamman a matakin farko, da wutar lantarki da ruwan sha domin habaka tattalin arzki da samar da ayyukan yi ga yan kasar.

Kwamitin ya kuma amince da ajiye wani bangare na kudin da ake rabawa a kowane wata domin takaita tasirin aeruwar shiga da za a iya samu sakamakon matakan cire tallatin mai da daidata farashin dala tare da hauhawar farashin kayayyaki za su iya haifarwa.

Kwamitin ya ce, daga cikin naira tiliyan 1.9 na kudin shigar da aka samu a watan Yunin 2023, naira biliyan 907 ne kawai za a raba tsakanin matakan gwamnatin kasar uku, yayin da za a ajiye naira biyan 790 a asusun.

Wadannan kudaden da za a riƙa ajiyewa za su taimaka wajen samar da asusun gina ababen more rayuwa tare da aiwatar da wasu abubuwa, domin tabbatar da an yi amfani da kudin tallafin wajen gina muhimman abubuwan ci gaba, domin inganta rayuwar yan kasar kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Haka kuma kwamitin ya yaba wa shugaban kasar bisa matakin cire tatafin man tare da bullo da matakai daban-daban na tallafa wa ‘yan kasar domin rage masu raɗadin cire tallafin.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp