Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da biyan Naira biliyan 12, domin biyan kudaden da ake kashewa ga Super Eagles da sauran kungiyoyin wasanni na kasa daban-daban.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka fitar a shafin X na Cibiyar Yada Labarai ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Sanarwar ta ce, biyan kudin zai shafe watanni 15 na albashin manyan kociyan kungiyar, da biyan alawus-alawus da kuma alkawuran da ya kamata a yi wa manyan kungiyoyin kasa da kasa, mata, da kuma ‘yan kasa da shekara 20.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Shugaba @officialABAT ya amince da biyan N12billion na baya bayan nan ga kungiyoyin kwallon kafar Najeriya na wasanni daban-daban da suka hada da Super Eagles da sauransu.
“Biyan ya hada da cire albashin manyan kocin kungiyar na tsawon watanni 15, da biyan alawus-alawus da kuma alkawuran da ya shafi manyan kungiyoyin kasa da mata da kuma ‘yan kasa da shekara 20.
“Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan wasan Super Eagles na Najeriya ke shirin shiga gasar cin kofin nahiyar Afrika, wanda ake sa ran za a fara a karshen wannan watan.”