Babban jigon jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi aiki tare domin samar da kasa mai inganci ga kansu da kuma na gaba.
A yayin bikin ranar ma’aikata, shugaban jam’iyyar APC ya ce, yayin da al’ummar kasar ke murnar wannan rana, “mu ‘yan Najeriya mu sadaukar da kanmu ga makoma mai cike da fata.
A cikin wata sanarwa da ofishin yada labaransa ya fitar domin tunawa da ranar, Tinubu ya kuma bukaci kowa da kowa ya yi abin da ya dace, don shimfidawa tare da saukaka wa ma’aikatan Najeriya.
A yayin da muke yabawa da kuma murnar ma’aikacin Nijeriya a wannan rana, a matsayinmu na ‘yan Nijeriya, mu sadaukar da kanmu ga kyakkyawar makoma inda kokarin mu na daidaiku da na jama’a suka hade cikin jituwa, domin samar da ingantacciyar Nijeriya ga kanmu da kuma zuriya masu zuwa. Allah ya albarkaci ma’aikata. Allah ya taimaki Najeriya.”