fidelitybank

Tinubu ya ƙaddamar da jiragen yaƙi masu saukar ungulu

Date:

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya jaddada aniyarsa ta kawo ƙarshen mastalar tsaro a ƙasar ta hanyar ƙaddamar da wasu sabbin jirage masu saukar ungulu kirar T-129 ATAK guda biyu da kirar King Air 360ER Beechcraft a barikin sojin saman Najeriy da ke birnin Makurdi a jihar Benue..

Da yake magana ta bakin mataimakin shugaban kasa Sanata Kashim Shettima, shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwar sayen waɗannan sabbin jiragen masu saukar ungulu domin inganta yaƙin da rundunar sojojin saman Najeriya ke yi a ƙasar da yankin yammacin Afirka.

Badaru Abubakar, ministan tsaro ya yaba wa ƙoƙarin shugaba Tinubu na mayar da zaman lafiya a fadin ƙasar, ya kuma gode masa bisa jajircewarsa da goyon bayan da yake bai wa rundunar sojin ƙasar duk da kalubalen da take fuskanta.

Ministan ya jaddada mahimmancin bin jadawali da aiwatar da tsare-tsare masu inganci don tabbatar da kyakkyawan aikin sabbin jiragen da aka sayo, tare da yin daidai da manufar shugaban kasa na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaba.

A yayin da yake jaddada mahimmancin wadannan sauye-sauye da aka samu, babban hafsan sojin sama, Hasan Abubakar, ya bayyana shirin rundunar sojin saman Najeriya na kaddamar da sabbin jiragen guda 46 na nau’uka iri-iri a cikin watanni 18 masu zuwa da wani babban sauyin a tsarin tsaron.

Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa, duk da cewa NAF na gudanar da ayyukanta ta kowane fanni, ba za ta huta ba har sai ta kawo karshen matsalar tsaro don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin ƴan Najeriya.

Daga nan, shugaban ya bukaci daukacin ‘yan Najeriya da su riƙe imani da fatan ci gaban ƙasar

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp