fidelitybank

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Date:

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce Najeriya na cikin wani mawuyacin hali a shekarar 2022, sakamakon fuskantar matsaloli da dama da ke barazana ga haɗin-kai, ɗorewar zaman lafiya da kuma makomarta har sai da shugaba Bola Tinubu ya zo ya cece ta bayan hawa mulki a shekarar 2023.

Ribadu ya bayyana haka ne a wani jawabi a taron kwalejin horas da sojoji ta Najeriya, inda ya bayyana lamarin da mai muni – inda sassan ƙasar duka suka shiga cikin matsalolin rashin tsaro.

Ya ce kafin zuwan Tinubu kan mulki matsaloli sun dabaibaye ƙasar – kama daga ayyukan masu ta da ƙayar-baya a arewa maso gabas sai kuma matsalar ƴanbindiga a arewa maso yamma, ta da zaune tsaye a yankin Neja Delta da kuma masu fafutukar ɓallewa a kudu maso gabashin ƙasar.

Ribadu ya ƙara tabbatar da hoɓɓasar da gwamnatin Tinubu take yi wajen ganin ta magancew matsalolin tsaro da ta gada.

A cewarsa, an ɗauki tsauraran matakai wajen dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Ya ce ƙoƙarin da gwamnati take yi wajen yaƙi da masu ta da ƙayar-baya ya kai kashe sama da ƴan ta’adda 13,500, yayin da sama da mayakan Boko Haram da na ISWAP 124,000 haɗe da iyalansu ne suka miƙa.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaƙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ƙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp