fidelitybank

Tinubu ne zai magance matsalar Najeriya – Yuguda

Date:

Tsohon gwamnan jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda, ya ce, Bola Tinubu, zai magance matsalar cin hanci da rashawa yadda ya kamata idan aka zabe shi a matsayin shugaban Najeriya a 2023.

Yuguda ya bayyana hakan a shirin gidan talabijin na Channels, Sunrise Daily a ranar Litinin.

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama ya yarda cewa, a matsayinsa na tsohon dan jam’iyyar PDP ya ga manyan cin hanci da rashawa a cikin shekaru 16 na mulkin jam’iyyar, wanda gwamnatin yanzu ta gada.

Ya soki gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, inda ya ce ta gaza cika alkawarin da ta dauka na yaki da cin hanci da rashawa, duk da kokarin da ta yi.

Da yake karin haske, Yuguda, wanda jigo ne a jam’iyyar APC, ya ce yana da yakinin cewa da Tinubu a kan karagar mulki za a magance matsalar cin hanci da rashawa.

“Cin hanci da rashawa matsala ce da ta gada kuma tana kara ta’azzara ko muna so ko ba mu so sai ’yan Najeriya sun gane cewa cin hanci da rashawa ne ke kashe mu kuma za ta kashe mu a karshe. Kowa ya lalace, ina jin tsoro.

“Gwamnatin ba ta gaza ba saboda abin da aka gada ke nan. Ina cikin gwamnatin da ta gabata kuma na ga cin hanci da rashawa.

“Wannan gwamnati ta zo ne da niyyar yaki da cin hanci da rashawa amma ba mu san irin nakiyoyin da aka binne a kan hanyarsu ta nakasa ba.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp