fidelitybank

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Date:

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi shugaba, Bola Tinubu da yunƙurin tauye haƙƙin ma’aikata, tare da hana su bayyana halin ƙuncin rayuwa da suke ciki.

Atiku ya bayyana cewa janye tallafin man fetur da Tinubu ya yi a ranar rantsar da shi ne ya haifar a matsalar tattalin arziki a ƙasar, wanda a cewarsa ya jefa masu ƙaramin ƙarfi a ƙasar cikin yunwa da rashin tabbas.

Ya ce domin Tinubu ya yi yunƙurin rage raɗaɗin da ƴankasar ke ciki ne ta hanyar ɗaukar alƙawarin ƙara albashi ga ma’aikatan ƙasar, “amma alƙawarin, kamar sauran alƙawura da ya ɗauka, sai da aka yi wata 10 kafin aka samu matsaya a sabon mafi ƙarancin albashi.”

A cewarsa, ya kamata ne gwamnati ta biya bashin cikon albashin na wata goma, “amma sai na wata shida kawai gwamnatin ta biya. Ke na ma’aikatan suna bin bashin cikon albashi na wata huɗu.

Atiku ya zargi gwamnatin da amfani da ƙarfi wajen “hana furta albarkacin baki maimakon neman matsaya ta hanyar tattaunawa.”

“Mako biyu da suka gabata an kama tare da tsare Andrewa Uche Emelieze saboda ya yi yunƙurin shirya zanga-zangar lumana. Cigaba da tsare ba ƙaramin cin fuska ba ne ga dimokuraɗiyyar Najeriya, har da cin fuska ga dukkan ma’aikatan ƙasar.

“Ya kamata a fahimci cewa ba a isa a doki ma’aikatan Najeriya sannan a hana su kuka ba, ballantana a musu barazana ko a manta da buƙatunsu. Lallai matsain tattalin arzikin da ake ciki a Najeriya gaskiya ne, kuma yunwa na ƙara katutu, wanda hakan ya sa gwamnati matakan gyara ya kamata ta ɗauka, ba daƙile masu magana ba.”

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da Ɗumi-Ɗumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp