fidelitybank

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Date:

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi shugaba, Bola Tinubu da yunƙurin tauye haƙƙin ma’aikata, tare da hana su bayyana halin ƙuncin rayuwa da suke ciki.

Atiku ya bayyana cewa janye tallafin man fetur da Tinubu ya yi a ranar rantsar da shi ne ya haifar a matsalar tattalin arziki a ƙasar, wanda a cewarsa ya jefa masu ƙaramin ƙarfi a ƙasar cikin yunwa da rashin tabbas.

Ya ce domin Tinubu ya yi yunƙurin rage raɗaɗin da ƴankasar ke ciki ne ta hanyar ɗaukar alƙawarin ƙara albashi ga ma’aikatan ƙasar, “amma alƙawarin, kamar sauran alƙawura da ya ɗauka, sai da aka yi wata 10 kafin aka samu matsaya a sabon mafi ƙarancin albashi.”

A cewarsa, ya kamata ne gwamnati ta biya bashin cikon albashin na wata goma, “amma sai na wata shida kawai gwamnatin ta biya. Ke na ma’aikatan suna bin bashin cikon albashi na wata huɗu.

Atiku ya zargi gwamnatin da amfani da ƙarfi wajen “hana furta albarkacin baki maimakon neman matsaya ta hanyar tattaunawa.”

“Mako biyu da suka gabata an kama tare da tsare Andrewa Uche Emelieze saboda ya yi yunƙurin shirya zanga-zangar lumana. Cigaba da tsare ba ƙaramin cin fuska ba ne ga dimokuraɗiyyar Najeriya, har da cin fuska ga dukkan ma’aikatan ƙasar.

“Ya kamata a fahimci cewa ba a isa a doki ma’aikatan Najeriya sannan a hana su kuka ba, ballantana a musu barazana ko a manta da buƙatunsu. Lallai matsain tattalin arzikin da ake ciki a Najeriya gaskiya ne, kuma yunwa na ƙara katutu, wanda hakan ya sa gwamnati matakan gyara ya kamata ta ɗauka, ba daƙile masu magana ba.”

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp