fidelitybank

Tinubu na yin rikon sakainar kashi a gwamnatinsa – Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Alhaji Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da yin rikon sakainar kashi na yin watsi da batun gaskiya.

Atiku ya ce gwamnatin Tinubu ta yi biris da al’amuran da suka shafi bin ka’ida wajen gudanar da ayyukan gwamnati.

Da yake aikawa a kan X, tsohon Mataimakin Shugaban kasar ya ce bashin dala biliyan 3.3 na NNPCL da ba a warware ba, shaida ce ga matsalolin cin hanci da rashawa da gwamnatin Tinubu.

A cewar Atiku: “Gwamnatin tarayya mai ci a halin yanzu tana da tarihin rashin kula da al’amuran da suka shafi gaskiya da adalci a harkokin gudanar da gwamnati.

“Bayan nan badakalar biyan bashin dala biliyan 3.3 na NNPCPL da ba a warware ba, inda a yanzu ake sa ran Najeriya za ta biya dala biliyan 12, ya kasance babban misali.

“Dole ne gwamnatin Tinubu ta magance wadannan manyan laifukan cin hanci da rashawa a fili.

“Majalisar kasa, a matsayinta na zababbun wakilan jama’a, wajibi ne a tsarin mulkin kasa ta samar da doka don samar da zaman lafiya, oda, da shugabanci nagari na al’ummarmu, ba tare da hada baki da gurbatattun mutane ba.

“Rashin yin haka da dagewa a cikin musantawa zai tabbatar da hadin kai da gwamnati ke yi a cikin rashin adalci a hukumance.-AA”

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp