Kungiyar Kwadago ta kasa NLC, ta tabbatar da cewa jami’an tsaro na farin kaya, DSS sun kama shugabanta, Joe Ajaero a ranar Litinin.
NLC ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar ta hannun asusun ta na X ranar Litinin.
NLC ta bayyana kamen a matsayin cin zarafi ga ma’aikatan Najeriya da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi.
“Ana ci gaba da cin zarafin ma’aikatan Najeriya. “Shugaban kungiyar NLC, Comrade Joe Ajaero, jami’an DSS ne suka kama shi suka yi awon gaba da shi a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe, Abuja, da safiyar yau a hanyarsa ta zuwa taron TUC United Kingdom, kuma yanzu haka yana tsare a ofishin NSA. ”, sanarwar ta kara da cewa.
DSS sun kama Ajaero a filin jirgin Nnamdi Azikiwe, Abuja.