Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya aike wa majalisar dattawa da buƙata inda yake neman izini domin karɓo bashin dala biliyan 21.5 daga ƙasashen waje da kuma naira biliyan 758 daga cikin gida.
Ana sa ran za a yi amfani da kuɗin wajen aiwatar da muhimman ayyuka kamar gyaran hanyoyi da kiwon lafiya da ilimi da samar da ruwan sha da kuma biyan tsoffin ma’aikata haƙƙoƙin fansho da ake bin su a ƙarƙashin tsarin Fansho na Gwamnati
Majalisar ta tura buƙatar zuwa kwamitinta mai kula da lamurran bashi na cikin gida da na waje, wanda ake sa ran zai kawo rahoto cikin makonni biyu.
Haka kuma, Shugaban ya buƙaci a ba shi damar cin bashin ƙarin dala biliyan biyu daga kasuwar cikin gida domin saka jari a wasu sassa masu muhimmanci na tattalin arziƙi wanda shi ma majalisar za ta tura zuwa ga kwamitin basussuka na gida da waje domin nazari.
A baya, Tinubu ya rubuta wa majalisar yana neman amincewa da sabon shirin rancen kuɗi na shekarar 2025 zuwa 2026.