Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce, shugaban Najeriya, Bola Tinubu, na kan wani yunkuri na kawo sauyi a Najeriya kamar yadda ya yi a lokacin da yake gwamnan jihar Legas.
Tinubu a halin yanzu yana kasar Faransa inda ya isa kasar turai a yammacin Laraba domin ziyarar aiki.
Da yake magana a wani liyafar cin abincin dare a Paris, babban birnin kasar Faransa, a ranar Alhamis, Macron ya ce Tinubu “ya ci mulkin soja”, a cewar wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai da dabaru.
“Najeriya babbar kasa ce mai hazaka da matasa. ‘Yan Najeriya da dama sun yi fice a ayyukan da suka zaba,” inji shi.
Da yake mayar da martani, Tinubu ya ce abin burgewa ne yadda Faransa karkashin jagorancin Macron ke son yin aiki tare da Najeriya.
Tinubu ya nanata cewa Najeriya za ta kyautata alaka da Faransa.
Ya ce, “Game da tattalin arzikin Najeriya, kamar yadda ka fada, mun gudanar da wani gagarumin sauyi, kuma babu waiwaye.
“Yana da amfani ga dukkanin nahiyar da ba mu ci gaba a baya ba. Dole ne mu jajirce don gaba tare da himma da kyakkyawan fata. Kuma tare da jajircewar kakannin mu na kafa.
“Shugaba Macron, duk kokarin da kuke yi game da Afirka, na yi alkawarin ba za ku zama a banza ba.
“Kun buɗe kofofin ku don saka hannun jari ga abokanmu da ’yan’uwanmu a nan. Ina iya ganin Aliko Dangote, Aig Imoukhuede, da Tony Elumelu a nan. Kuna da tunanin abokan ku a Najeriya. Kun nemi Mike Adenuga a safiyar yau. Na gode.”