fidelitybank

Tinubu na fuskantar matsin lamba da ya dakatar da Betta Edu

Date:

Kwanaki ƙalilan bayan hukumar EFCC ta gayyaci tsohuwar ministar jin-ƙai, Sadiya Umar Farouk, kan zargin ɓarnatar da wasu kuɗaɗe, sai ga shi sabuwar ministan jin-ƙan, Betta Edu na ƙoƙarin wanke kanta daga zargin sabuwar badaƙala a ma’aikatar.

Hakan na zuwa ne bayan fitar wata takardar biyan kuɗi da ministar ta aike wa ofishin babbar akanta janar da ƙasar, inda a ciki take buƙatar a tura zunzurutun kuɗi har naira miliyan 585, 189,500, don biyan tallafi, a wani ɓangare na tallafa wa masu tsananin buƙatar tallafi a wasu jihohin kasar huɗ.

To sai dai wani abu da ya ja hankali game da biyan kuɗaden shi ne sunan asusun bankin da aka biya kuɗin na wata mata ce mai suna Onlyelu Bridget Mojso.

Tuni dai ofishin babar akanta janar ta ƙasar ya ce ba ya biyan kuɗin gudanar da wani aiki na gwamnati a asusun wani mutum.

Wannan batu dai ya janyo ce-ce-ku-ce a ƙasar musamman a shafukan sada zumunta inda mutane da dama ke kiran shugaban kasar Bola Tinubu ya sauke ministar daga mukaminta

Wani mai amfani da shafin X mai suna Waspapping_ya ce ”idan har aka kai safiyar gobe Betta Edu na kan matsayinta, to za mu son cewa Bola Ahmed Tinubu bai shirya wa jagorantar ƙasar nan ba. Babu yadda za a yi ka dakatar da Halima Shehu sannan ka bar Betta Edu, wadda ake da manyan zarge-zarge a kanta ba, ka dakatar da ita yanzu, sannan ka bar EFCC su gayyaceta domin tuhumarta.

Shi ma wani mai amfani da shafin X mai suna TahaAdamy cewa ya yi ”Kamar Halima, ya kamata a dakatar da Betta Edu, a binciketa, sannan a gurfanar da ita idan an same ta da laifi. Ya kamata shugaban ƙasa ya rushe ma’aikatar jin-ƙai, saboda tana neman zama wata matattarar cin hanci ga mutanen da suka jagorance ta a baya da kuma yanzu, a ƙarfafa hukumar NEMA don aiwatar da ayyukan hukumar.

A nata ɓangare ministar jin-ƙai Betta Edu ya musanta zargin, tana mai bayyana shi a matsayin maras tushe balle makama.

Ministar ta kuma ce wannan batun tuggun masu kawo ruɗani ne da ke ƙoƙarin ganin sun dankwafar da ƙoƙarin da ma’aikatarta ke yi wajen kawar da cin hanci da rashawa.

A farkon wannan makon ne hukumar EFCC ta gayyaci dakatacciyar shugabar hukumar bayar da tallafin dogaro da kai ta Najeriya, NSIPA, Hajiya Halima Shehu kan zargin badaƙalar kuɗaɗe.

Rahotonni na cewa Hajiya Halima ta tra wasu kudi kimanin naira biliyan 40 daga asusun hukumar NSIPA zuwa wasu asusu mallakin wata mata da kuma wani kamfani na daban.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp