fidelitybank

Tinubu na ƙwato kuɗaɗen da aka sace a gwamnatocin baya – Sarkin Minna

Date:

Sarkin Minna, Alhaji Umar Farouk Bahago ya ce shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi bakin ƙoƙarinsa wajen ƙwato kuɗaɗen da aka sace a gwamnatocin baya, amma ƴan Najeriya ba su gane ba.

Sarkin ya bayyana hakan a taron wayar da kan ƴan ƙasa a kan tallafin da Gwamnatin Tarayya ke yi a jihohin ƙasar, wanda ofishin Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Al’umma ya shirya a Minna na Jihar Neja.

Sarkin wanda Hadinin Minna, Alhaji Maukudi Achaza ya wakilta, ya ce Tinubu na bakin ƙoƙarinsa wajen magance matsalar cin hancin da rashawar da aka yi a baya.

Ya ce tallafin da gwamnatin Tinubu ke yi, yawancin ƴan ƙasar ba su sani ba saboda masu magana da yawun gwamnatin ba sa yaɗa ayyukan yadda ya kamata musamman wajen yin magana da harshen da mutanen ke ji.

“An sace maƙudan kuɗaɗe da dama a gwamnatocin baya, wanda gwamnatin yanzu ke ƙoƙarin ƙwatowa, amma mutane da dama ba su fahimta ba. Sannan tun bayan janye tallafin man fetur, an gudanar da abubuwa da dama domin rage raɗaɗin da ƴan ƙasa suka shiga. Yana da kyau gwamnati ta riƙa wayar da kan mutane a kan shirye-shiryenta a harshen da suke ji,” in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp