fidelitybank

Tinubu kar ka zama irin Buhari na ƙin tattauna wa ƴan bindiga – Gumi

Date:

A wani yunkuri na ganin an sako ‘yan Najeriya da aka sace, babban malamin addinin musuluncin nan, Sheikh Ahmad Gumi, ya bayyana aniyarsa ta samar da cikakkiyar tattaunawa tsakanin gwamnatin tarayya da ‘yan bindiga.

Sheikh Gumi ya bukaci gwamnatin shugaba Bola Tinubu da kada ta sake maimaita kuskuren da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi, wanda ya ki tattaunawa da ‘yan fashi.

Ya mayar da martani ne kan kin amincewa da gwamnatin jihar Kaduna ta yi da ‘yan bindigar da suka sace ‘yan makaranta 287 a Sakandaren gwamnatin Kuriga da kuma makarantun firamare a karamar hukumar Chikun.

A makon da ya gabata, ‘yan bindiga sun sace dalibai sama da 280 a makarantar firamare ta Kuriga, da kuma gwamnati.

Da yake mayar da martani, Gumi, a cikin wata sanarwa ya ce: “Matsayin gwamnati na rashin tattaunawa da ‘yan fashin wani matsayi ne mara dadi. Shawarata ita ce gwamnati ta tattauna da ’yan fashi ba wai kawai a sace yaran nan na makarantar Kuriga ba, har ma da dukkan al’amura.

“Har ila yau, ya kamata gwamnati ta yi amfani da hanyar da ta bi wajen sakin fasinjojin da aka sace a jirgin Abuja zuwa Kaduna a shekarar 2022 don sako yaran makarantar Kuriga da sauran su.

“A shirye nake in jagoranci cikakkiyar tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan bindiga. Ya zama wajibi a gare ni in yi haka domin zaman lafiya.

“Ina fata gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu mai ci za ta saurara ta hanyar tattaunawa da ‘yan bindiga saboda tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta ki yin hakan.”

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp