fidelitybank

Tinubu ka yi taka-tsantsan a kan Nijar – Gamayyar Ƙwararru

Date:

Wata gamayyar ƙwararru ƴan Najeriya, ta yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi taka-tsantsan wajen ɗaukar matakan mayar da jamhuriyar Nijar kan turbar dimokraɗiyya, bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa shugaba Mohamed Bazoum.

A wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da gamayyar ta aika wa Shugaba Tinubu, ta ce akwai buƙatar Najeriya ta zamo mai sara tana duban bakin gatari game da matsayarta a kan abin da ke faruwa a Nijar, musamman bisa la’akari da daɗaɗɗiyar dangantaka mai kyau tsakanin ƙasashen biyu, aminan juna.

Shugaban na Najeriya, Bola Tinubu, shi ne ke jagorantar Ƙungiyar Raya Ƙasashen Afirka ta Yamma wato Ecowas da ta bai wa sojoji masu mulki a Nijar wa’adin kwana bakwai don su mayar da mulki hannun hamɓararren shugaban ƙasa Bazoum Mohamed ko kuma ta ɗauki matakin amfani da ƙarfi a kansu.

Gamayyar wadda ta ƙunshi ƙwararru daga ɓangarori daban-daban na rayuwa, ta bi sahun Ecowas da sauran ƙasashen da ƙungiyoyin duniya wajen yin Allah-wadai da juyin mulkin na Nijar, amma ta ce hanyar lumana ta fi dacewa a bi wajen warware matsalar.

Ta jaddada goyon bayanta ga yin amfani da sarakuna da malaman addini da kuma ƙungiyoyi wajen tuntuɓa da neman maslaha tsakanin sojojin da suka ƙwace mulki a Nijar don kaucewa duk wani abu da zai ta’azzara rikici.

Haka kuma, gamayyar ta fargar da Shugaba Tinubu a kan buƙatar inganta hanyar fitar da bayanai game da matakan da ake ɗauka a kan Nijar don kaucewa faɗawa tarkon masu yaɗa labaran bogi kan matsayar Najeriya da ma shugaba Tinubu game da wannan dambarwa

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp