fidelitybank

Tinubu ka yi taka-tsantsan a kan Nijar – Gamayyar Ƙwararru

Date:

Wata gamayyar ƙwararru ƴan Najeriya, ta yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi taka-tsantsan wajen ɗaukar matakan mayar da jamhuriyar Nijar kan turbar dimokraɗiyya, bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa shugaba Mohamed Bazoum.

A wata buɗaɗɗiyar wasiƙa da gamayyar ta aika wa Shugaba Tinubu, ta ce akwai buƙatar Najeriya ta zamo mai sara tana duban bakin gatari game da matsayarta a kan abin da ke faruwa a Nijar, musamman bisa la’akari da daɗaɗɗiyar dangantaka mai kyau tsakanin ƙasashen biyu, aminan juna.

Shugaban na Najeriya, Bola Tinubu, shi ne ke jagorantar Ƙungiyar Raya Ƙasashen Afirka ta Yamma wato Ecowas da ta bai wa sojoji masu mulki a Nijar wa’adin kwana bakwai don su mayar da mulki hannun hamɓararren shugaban ƙasa Bazoum Mohamed ko kuma ta ɗauki matakin amfani da ƙarfi a kansu.

Gamayyar wadda ta ƙunshi ƙwararru daga ɓangarori daban-daban na rayuwa, ta bi sahun Ecowas da sauran ƙasashen da ƙungiyoyin duniya wajen yin Allah-wadai da juyin mulkin na Nijar, amma ta ce hanyar lumana ta fi dacewa a bi wajen warware matsalar.

Ta jaddada goyon bayanta ga yin amfani da sarakuna da malaman addini da kuma ƙungiyoyi wajen tuntuɓa da neman maslaha tsakanin sojojin da suka ƙwace mulki a Nijar don kaucewa duk wani abu da zai ta’azzara rikici.

Haka kuma, gamayyar ta fargar da Shugaba Tinubu a kan buƙatar inganta hanyar fitar da bayanai game da matakan da ake ɗauka a kan Nijar don kaucewa faɗawa tarkon masu yaɗa labaran bogi kan matsayar Najeriya da ma shugaba Tinubu game da wannan dambarwa

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...
X whatsapp