fidelitybank

Tinubu ka sauke duk wanda ya kasa cika aikin sa – El-Rufa’i

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya shawarci shugaban kasa Bola Tinubu da ya sauke duk wanda ya nada wanda ya kasa cika aikin sa.

El-Rufai ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Maiduguri a ranar Litinin, inda ya bukaci shugaban kasar da ya kuma duba yiwuwar gyara wasu manufofinsa da ba sa samar da sakamakon da ake bukata.

“Kun nada mutum mukami kuma ba ya aiki yadda ake tsammani, ya kamata ku kasance da tawali’u don gaya masa cewa ina bukatan wanda ya fi ni, je ku yi wani abu daban,” in ji El-Rufai.

El-Rufai ya kuma yi kira da a yi addu’a da goyon bayan ’yan kasa ga gwamnati a yunkurinta na ganin ta dawo da al’amura.

“Abin da ya kamata mu yi a matsayinmu na ’yan kasa shi ne mu yi wa shugabanninmu addu’a don Allah Ya yi musu jagora su gani ko su yi abin da ya dace.

“Domin Allah ya ba su tawali’u su juyar da kansu a lokacin da ya dace kuma su yi abin da ya dace; haka al’umma ke ci gaba,” in ji shi.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp