fidelitybank

Tinubu ka janye ƙudurin dokar haraji – Kungiyar Kwadago

Date:

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya, NLC ta buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya janye ƙudurin dokar haraji da ya gabatar ga majalisar dokokin ƙasar domin bayar da dama kan sake yin nazari.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a cikin saƙonta na sabuwar shekara, wanda shugabanta Joe Ajaero ya fitar a yau Laraba.

Saƙon ya ce “domin samar da tsarin dimokuraɗiyya mai tabbatar da ci gaban ƙasa, dole ne mu gina tsari kan tubalin tattaunawa, da bai wa masu ruwa da tsaki damar tsoma baki a harkar gina ƙasa.

“A kan haka ne muke sake yin kira ga gwamnatin tarayya da ta janye ƙudurin harajin da yanzu haka ke a gaban Majalisar dokoki domin bai wa duk ɓangarorin da suka dace bayar da gudumawa a kansa”.

Sanarwar ta ce ƙungiyar, ita ma za ta so ta taimaka wajen samar da kyakkyawan tsarin haraji wanda zai samu karɓuwa a tsakanin al’umma, kuma ya taimaka wajen ci gaban ƙasa.

Batun ƙudurin harajin da Tinubu ya gabatar, na daga cikin manyan sauye-sauyen da sabon shugaban ƙasar ya bijiro da su tun bayan hawa mulki a shekara ta 2023.

Sai dai ƙudurin harajin ya fuskanci turjiya daga ɓangarori da dama na ƙasar, ciki har da Majalisar tattalin arziƙi ta ƙasar, da gwamnoni da kuma ƙungiyoyi.

Lamarin da ya tursasa wa Majalisar dokokin ƙasar jinkirta muhawara kan ƙudurin, yayin da shugaban ƙasar ya buƙaci ma’aikatar shari’a ta ƙasar ta haɗa hannu da majalisar domin warware ɓangarorin dokar da ake ganin su ne suka haifar da taƙaddama.

Sai dai a tattaunawarsa da kafafen yaɗa labaru sa’ilin hutun ƙarshen shekara a birnin Legas, wadda ita ce ta farko tun bayan hawa kan mulki, Tinubu ya sha alwashin tabbatar da ganin sabuwar dokar harajin ta fara aiki.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp