fidelitybank

Tinubu ka gaggauta umartar NNPCL su cire karin fetur – SERAP

Date:

Ƙungiyar SERAP mai fafutikar yaƙi da cin hanci a Najeriya ta buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya yi amfani da ”matsayinsa ya tilasta wa babban kamfanin mai na ƙasar, NNPCL ya gaggauta janye ƙarin farashin man fetur da ƙungiyar ta kira ‘wanda ya saɓa wa doka’.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ranar Lahadi ta ce ƙarin kuɗin man fetur ɗin ya saɓa wa kundin tsarin mulki tare da dokokin ƙasar game da kare haƙƙin bil-adama.

SERAP ta kuma buƙaci shugaba Tinubu ya ”umarci babban lauyan gwamnatin ƙasar, Lateef Fagbemi, SAN da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa su binciki zarge-zargen cin hanci da almabazzaranci a ake yi wa kamfanin NNPCL.

Ciki har da kuɗin tallafin ƙwatar kai (bailout), na dala miliyan 300 da kamfanin ya karɓa daga gwamnatin tarayya a watan Agustan da ya gabata, da kuma zargin kamfanin da rashin saka ribar mai a asusun gwamnati.

SERAP ta ce “ya kamata a gurfanar da waɗanda ake zargi da aikata laifi a NNPCL a gaban kotu domin su fuskanci hukunci, idan har an same su da laifi, tare da ƙwato duk abin da suka sata”.

ƙungiyar ta kara da cewa cin hanci da rashawa da ake zargin samu fannin man fetur da kuma kashe kuɗin gwamnati ba bisa ƙai’da ba, da kuma yin ƙunbiya-ƙunbiya ko rufa-rufa sun taimaka wajen ƙarin taɓarɓarewar al’amura a kamfanin, wanda kuma shi ke haifar da ƙarin kuɗin man fetur a koyaushe a ƙasar.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp