fidelitybank

Tinubu ka gaggauta janyewar da ka yi wa Fubara – Gwamnonin PDP

Date:

Gwamnonin jam’iyyar PDP sun buƙaci Shugaban kasa, Bola Tinubu da ya janye dakatarwar da ya yi wa gwamnan Rivers Siminalayi Fubara.

Ƙungiyar Gwamnonin ta PDP ta bayyana dakatarwar da aka yi wa Fubara a matsayin “babban kuskure” sannan mummunan mataki ne da zai haifar da koma-baya.”

A ranar Talata da daddare ne Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan jihar Rivers sakamakon ƙiƙi-ƙaƙar siyasa da aka daɗe ana gani a jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya.

Shugaban ya kuma dakatar da Fubara da mataimakinsa da ƴanmajalisar dokokin jihar tare kuma da naɗa Ibok-Ete Ibas, tsohon soji mai muƙamin vice-admiral, a matsayin wanda zai ja ragamar al’amuran jihar.

Cikin wata sanarwa ranar Laraba, Bala Mohammed wanda shi ne gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban kungiyar gwamnonin PDP, ya ce ayyana dokar ta-ɓacin a Rivers abin damuwa ne kan makomar jihar.

Gwamna Bala Muhammad ya ce jan baki ya yi shiru da Tinubu ya yi kan rawar da Nyesom Wike, ministan Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja ke takawa a rikicin siyasar na Rivers kamar ba shi dama ce ya yi kiɗinsa kuma ya yi rawarsa.

Ya ce “Wike ya zama doka saboda yana yin abin da kake so. Yanzu mun sani. Wannan sam babu dattako, an nuna son kai da kuma rarraba kawuna,” in ji sanarwar.

Kungiyar gwamnonin ta PDP ta ce matakin ƙarara barazana ce ga dimokraɗiyyar Najeriya sannan zai ƙara rura wutar rikici a ƙasar tare da ƙara janyo rashin yarda da lalata tattalin arziki da kuma zaman lafiyar ƙasa baki ɗaya.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp