fidelitybank

Tinubu ka fito ka bayyana gaskiyar rayuwarka – Obi

Date:

Ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar LP, Peter Obi, ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya fito ya fayyace gaskiya game da rayuwarsa.

Obi ya bayyana haka ne a wata ganawa da manema labaru yau Laraba a birnin Abuja.

A lokacin ganawar, Peter Obi ya ce: “Ina kira gare shi (Tinubu) ba tare da ɓata lokaci ba ya yi abu mai sauƙi, ya bayyana wa al’ummar ƙasar da yake mulka ko shi wane ne domin kawar da duk wani shakku.”

“Ya kamata ya sanar da duniya asalin sunansa, da ƙasarsa da inda aka haife shi da iyayensa da makarantun sakandare da firamaren da ya halarta da jam’iar da ya halarta da kuma takardun shaidar kammala karatun.”

Hakan na zuwa ne ƙasa da mako guda bayan da ɗan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, a lokacin wani taron manema labaru ya yi zargin cewa Tinubu ya gabatar da takardun bogi domin tsayawa takarar shugaban ƙasa.

Batun asalin Bola Tinubu da karatunsa lamari ne da ke janyo ce-ce-ku-ce tun lokacin da shugaban na Najeriya ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa.

Tuni dai jami’ar jihar Chicago da ke Amurka, wadda Tinubu ya bayyana cewa ya halarta ta saki bayanai da suka tabbatar da cewa ya halarci makarantar, inda ya samu shaidar kammala karatun digiri.

Sai dai har yanzu ƴan takarar shugaban ƙasa na manyan jam’iyyun adawa biyu a zaɓen na watan Fabarairun 2023 na nuna shakku tare da cewa suna da shaidun da ke nuna cewa Tinubu ya yi amfani da takardun bogi domin samun damar yin takara

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp