fidelitybank

Tinubu ka bude mana iyakar Najeriya da Benin Oba Hammed

Date:

Oba Hameed Oyelude, Olowu na Kuta a karamar hukumar Ayedire ta jihar Osun, ya roki shugaban kasa Bola Tinubu da ya sake bude kan iyakar kasar da jamhuriyar Benin.

Oba Oyelude, wanda ya yi wannan roko a wata tattaunawa da ‘yan jarida a ranar Lahadi a fadarsa da ke Kuta, ya ce bude kan iyakar zai sauwaka wa ‘yan Najeriya matsalolin tattalin arziki.

“A lokacin da aka rufe iyakar Jamhuriyar Benin, gwamnatin tarayya tana kare tattalin arzikin kasar.

“Amma ina so in roki shugaban kasa ya duba yiwuwar sake bude kan iyaka don rage radadin ‘yan Najeriya,” in ji shi.

Ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su yi hakuri da shugaban kasar, yana mai cewa yana nufin alheri ga kasar ta hanyar cire tallafin man fetur.

“Ribar cire tallafin man fetur na zuwa, amma watakila ba nan take ba. Don haka ne ya kamata mu yi hakuri da Shugaban kasa.

“Bari mu baiwa wannan gwamnati lokaci. Ba shakka za mu isa wurin,” basaraken ya roki.

Ya bukaci Gwamnatin Tarayya da kada ta dauki dukkan shawarwari da manufofin Asusun Ba da Lamuni na Duniya, IMF.

Sarkin ya ce duk da cewa babu laifi wajen sanya ra’ayoyi da manufofin IMF a cikin gida, amma dole ne a yi hakan ta hanyar da za ta dace da kasar.

“Akwai koma bayan tattalin arziki kuma kalubale ne da muke fuskanta, amma na yi imanin za mu shawo kan lamarin a matsayin kasa,” in ji shi.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp