fidelitybank

Tinubu ka biya albashi mafi karanci na dubu 615 – NLC

Date:

Kungiyar ƙwadago ta Najeriya NLC ta gabatar da buƙatar ƙarin sabon albashi mafi karanci na N615,000 domin magance kalubalen tattalin arziki da tsadar rayuwa da ma’aikata ke fuskanta a Najeriya.

Shugaban kungiyar ne ya tabbatar da hakan ga gidan talabijin na Channel a ranar Lahadi.

An cimma sabon albashin N615,000 duk wata bayan tattaunawa tsakanin ƙungiyar kwadago ta NLC da TUC ne da nufin rage matsalolin kudi da ma’aikatan Najeriya ke fuskanta.

Ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce mafi karancin albashi na N30,000 a halin yanzu ba zai iya biyan buƙatun talakawan Najeriya ba, suna masu korafin cewa ba dukkan gwamnoni ne ke biyan albashin ma’aikata na yanzu ba wanda zai ƙare a watan Afrilu, shekaru biyar bayan sohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya rattaba hannu kan dokar mafi karancin albashi ba 2019 inda za a sake duba dokar duk bayan shekaru biyar.

Kungiyoyin NLC da TUC a lokuta daban-daban sun yi kira ga gwamnatin shugaba Bola Tinubu da ta gaggauta sake duba mafi ƙarancin albashin ma’aikata.

A farkon watan Janairu ne gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da wani kwamitin mutum 37 kan mafi karancin albashin ma’aikata na kasa.

Da farko dai ƙungiyar kwadago ta NLC ta sanar da naira miliyan ɗaya a matsayin sabon mafi karancin albashi, sakamakon hauhawar farashin kayayyaki a kasar da ya jefa mutane da dama cikin talauci.

Yayin da kuma TUC ta buƙaci naira 447,000 a matsayin sabon mafi karancin albashi na wata-wata ga kowane ma’aikaci, wanda daga baya kuma NLC ta bukaci N794,000 ga kowane ma’aikaci.

Amma ƙungiyoyin biyu, a wata sabuwar shawara ga gwamnati, sun buƙaci naira 615,000 a matsayin sabon mafi karancin albashin ma’aikata.

Kungiyoyin sun ce hauhawar farashin kayayyaki – wanda ya kai kashi 31.70 cikin 100 a watan Fabrairun 2024 ya shafi tsadar rayuwa ga matsakaitan ma’aikatan Najeriya.

Sun kuma lura da cewa gwamnonin jihohi za su iya biyan kowane ma’aikacin gwamnati albashi saboda a yanzu suna samun karin kudaden shiga kowane wata daga hukumar dake tattara da raba arziƙin ƙasa (RMAFC).

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp