fidelitybank

Tinubu ka bi mana kadin Ɗan mu ɗan shekara 6 – Iyayensa

Date:

Mahaifan wani yaro ɗan kimanin shekaru biyar da aka sace, sannan aka kashe a birnin Sakoto sun yi kira ga hukumomin tsaro na tarayyar Najeriya ƙungiyoyin kare hakkin bil adama, su bi musu kaɗin jinin ɗansu.

An dai sace yaron mai suna Ayman ne a daren ƙaramar sallah wato 29 da watan Maris a unguwarsu ta CBN Quarters Sokoto, sai bayan kwanaki 48 aka ga gawarsa cikin wani ramin ruwa wato Soakaway, a kusa da gidansu.

Mahaifin yaron Dakta Abubakar Hamza ya shaida wa BBC cewa an sace yaron ne bayan dawowa daga sallar la’asar, daga suka yi ta nema, sai wani ƙaramin yaro ya ce ai ya gan shi wasu sun saka shi cikin mota sun tafi da shi.

Ya ce bayan ƴan kwanaki sai wata mai suna Ummu ta ce masa ta son inda Ayman yake, wai an yi garkuwa da saurayin ƙawarta, wanda ya ce an tsare su tare da Ayman a yankin Kamba, ta kuma faɗa musu cewa za ta taimaka wajen dawo da yaron.

”To sai dai bayan da ta buƙaci kudi kuma muka ba ta sai maganar ta shirice, matar da riƙa yi mana gobe-gobe, har dai muka sanar wa hukumomi, suka kuma kamata, amma bayan bincike sun ce mana ƙarya take yi ba ta san inda Ayman yake ba”, in ji mahaifin yaron.

”Amma abin mamaki kwana biyu da suka wuce sai aka ganshi a cikin ramin ruwa (Soakaway)”.

Mahaifin yaron ya yi kira ga hukumomi su taimaka wajen bi masa kadin jinin ɗansa.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp