Mahaifan wani yaro ɗan kimanin shekaru biyar da aka sace, sannan aka kashe a birnin Sakoto sun yi kira ga hukumomin tsaro na tarayyar Najeriya ƙungiyoyin kare hakkin bil adama, su bi musu kaɗin jinin ɗansu.
An dai sace yaron mai suna Ayman ne a daren ƙaramar sallah wato 29 da watan Maris a unguwarsu ta CBN Quarters Sokoto, sai bayan kwanaki 48 aka ga gawarsa cikin wani ramin ruwa wato Soakaway, a kusa da gidansu.
Mahaifin yaron Dakta Abubakar Hamza ya shaida wa BBC cewa an sace yaron ne bayan dawowa daga sallar la’asar, daga suka yi ta nema, sai wani ƙaramin yaro ya ce ai ya gan shi wasu sun saka shi cikin mota sun tafi da shi.
Ya ce bayan ƴan kwanaki sai wata mai suna Ummu ta ce masa ta son inda Ayman yake, wai an yi garkuwa da saurayin ƙawarta, wanda ya ce an tsare su tare da Ayman a yankin Kamba, ta kuma faɗa musu cewa za ta taimaka wajen dawo da yaron.
”To sai dai bayan da ta buƙaci kudi kuma muka ba ta sai maganar ta shirice, matar da riƙa yi mana gobe-gobe, har dai muka sanar wa hukumomi, suka kuma kamata, amma bayan bincike sun ce mana ƙarya take yi ba ta san inda Ayman yake ba”, in ji mahaifin yaron.
”Amma abin mamaki kwana biyu da suka wuce sai aka ganshi a cikin ramin ruwa (Soakaway)”.
Mahaifin yaron ya yi kira ga hukumomi su taimaka wajen bi masa kadin jinin ɗansa.