fidelitybank

Tinubu ka bi mana kadin Ɗan mu ɗan shekara 6 – Iyayensa

Date:

Mahaifan wani yaro ɗan kimanin shekaru biyar da aka sace, sannan aka kashe a birnin Sakoto sun yi kira ga hukumomin tsaro na tarayyar Najeriya ƙungiyoyin kare hakkin bil adama, su bi musu kaɗin jinin ɗansu.

An dai sace yaron mai suna Ayman ne a daren ƙaramar sallah wato 29 da watan Maris a unguwarsu ta CBN Quarters Sokoto, sai bayan kwanaki 48 aka ga gawarsa cikin wani ramin ruwa wato Soakaway, a kusa da gidansu.

Mahaifin yaron Dakta Abubakar Hamza ya shaida wa BBC cewa an sace yaron ne bayan dawowa daga sallar la’asar, daga suka yi ta nema, sai wani ƙaramin yaro ya ce ai ya gan shi wasu sun saka shi cikin mota sun tafi da shi.

Ya ce bayan ƴan kwanaki sai wata mai suna Ummu ta ce masa ta son inda Ayman yake, wai an yi garkuwa da saurayin ƙawarta, wanda ya ce an tsare su tare da Ayman a yankin Kamba, ta kuma faɗa musu cewa za ta taimaka wajen dawo da yaron.

”To sai dai bayan da ta buƙaci kudi kuma muka ba ta sai maganar ta shirice, matar da riƙa yi mana gobe-gobe, har dai muka sanar wa hukumomi, suka kuma kamata, amma bayan bincike sun ce mana ƙarya take yi ba ta san inda Ayman yake ba”, in ji mahaifin yaron.

”Amma abin mamaki kwana biyu da suka wuce sai aka ganshi a cikin ramin ruwa (Soakaway)”.

Mahaifin yaron ya yi kira ga hukumomi su taimaka wajen bi masa kadin jinin ɗansa.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp