fidelitybank

Tinubu ka ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a Najeriya – CCC

Date:

Cibiyar tattarawa da yaɗa bayanai kan rikice-rikice (CCC) ta yi gargaɗin cewa garkuwa da mutane na ƙaruwa a Najeriya, inda ta yi kira ga Gwamnatin Tarayyarv ƙasar da ta ayyana dokar ta-ɓaci domin magance matsalar.

Shugaban CCC, Manjo Janar Chris Olukolade, mai ritaya, a wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa matsalolin za su iya ta’azzara idan ba a yi abin da ya dace ba, wanda hakan zai ƙara jefa rayuwar al’umma cikin matsala da ƙara taɓarɓarar da matsalar tsaro.

Sanarwar ta ƙara da cewa garkuwa da mutane ta rikiɗe zuwa wata babbar harka ta kasuwanci, inda ƙungiyoyin ta’addanci ke amfani da lamarin domin samun kuɗin shiga.

“Sace mutum da aka yi na kwana-nan shi ne sace basarake a Masarautar Sokoto, da sace ɗaliban jami’a masu karatun kiwon lafiya guda 20, waɗanda aka sako daga baya, da kuma cigaba da riƙe Dokta Ganiat Popoola.”

CCC ta bayar da shawarar a tunkari matsalar da ƙarfi ta hanyar amfani da fasahar zamani da bibiyar harkokin jami’an tsaro da kuma magance matsalolin rayuwa da mutane suke fuskanta.

Haka kuma cibiyar ta yi kira ga ƙasashen waje da su taimaka wa Najeriya wajen yaƙi da matsalar.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp