Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira shugaba Tinubu da manyan muƙarraban gwamnatinsa da su mayar da hankali wajen ganin sun kyautata rayuwar ƴan Najeriya maimakon gangamin yaƙin neman a sake zaɓen Tinubu a 2027, inda a cewar ƙungiyar hakan ya yi wuri.
A wata sanarwa da kakakin ƙungiyar na ƙasa, Farfesa Tukur Muhammad-Baba ta taya Musulmi murnanr Babbar Sallah, ƙungiyar ta bayyana rashin jin daɗinta dangane da taɓarɓarewar tsaro da tsadar rayuwa da rashin wutar lantarki da matsalolin lafiya, ilimi da karyewar darajar Naira da tashin farashin kayan abinci.
Ƙungiyar ta kuma nuna takaicinta yadda duk da irin waɗannan ƙalubale amma jam’iyyar APC ta fi mayar da hankali kan gangamin yaƙin neman zaɓen Tinubun a 2027.
Idan dai ba a manta ba a watan da ya gabata ne dukkanin gwamnaonin jam’iyyar APC 22 a faɗin ƙasar suka amince da cewa Bola Tinubu ne ɗan takararsu a zaɓen 2027 mai zuwa, wani al’amari da ya janyo cece-kuce a Najeriya.