fidelitybank

Tinubu dan kishin Dimokradiyya ne – Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya kwatanta zababben shugaban kasa da aka zaɓa Bola Tinubu a matsayin ɗan kishin dimokuraɗiyya.

Gwamna Ganduje ya bayyana haka ne yayin taya Tinubu murnar lashe zaɓen shugaban Najeriya da ya yi a aɓen ranar 25 ga watan Febrairu.

A cikin wata sanarwa da sakataren watsa labaru ga gwamnan Abba Anwar ya fitar, Ganduje ya yaba da irin jajircewar Tinubu da kuma na sauran mutane da suka tsaya wajen ganin sun cimma nasara.

“Bola Ahmed Tinubu jajirtaccen mutum ne da ke son ci gaban ƙasa da kuma al’umma saboda irin ayyuka da ya yi a faɗin ƙasa,” in ji Gwamnan.

Ganduje ya ce jajircewar da Tinubu ya yi na tsawon shekaru wajen ganin tabbatuwar dimokuraɗiyya a Najeriya, shi ya sa suka ga ya dace ya mulki ƙasar nan.

Ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa zaɓaɓɓen shugaban ƙasar zai yi aiki tukuru waje ganin ya shawo kan matsaloli da ƙasar ke fuskanta.

Gwamna Ganduje ya gode wa mambobin jam’iyyarsu da kuma dukkan waɗanda suka jajirce wajen samun nasararsu.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp