fidelitybank

Tinubu da Shettima sun gana da gwamnoni a kan sabon albashi

Date:

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa Kassim Shettima, sun gana da gwamnonin jihohi 36, har da ministoci game da sabon albashi mafi karanci ga ma’aikata da sauran batutuwan da suka shafi tattalin arziki.

Shugaba Tinubu da gwamnoni sun gana a taron majalisar tattalin arziki ta kasa karo na 141 da aka gudanar a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ne ya jagoranci tattaunawar da gwamnoni da mataimakansu da kuma ministoci kafin isowar shugaban.

Taron ya zo ne kwanaki biyu bayan da majalisar zartaswar gwamnatin tarayya ta jinginar da batun mafi kankantar albashin domin ba da dama a kara yin tuntuba.

A ranar Laraba ne dai gwamnoni karkashin kungiyar gwamnoni ta kasa suka gana a Abuja, inda suka bai wa yan kasa tabbacin cewa tattaunawar da ake ci gaba da yi tsakanin gwamnati da bangarori masu zaman kansu da kuma kungiyar kwadago zai yi tasiri.

Ana sa ran shugaba Tinubu zai dauki mataki kan shawarar Naira dubu 62,000 da gwamnati ta bayar da kuma bukatar yan kwadago ta neman mafi karancin albashi ya zama Naira 250,000.

 

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp