Yusuf Datti Baba-Ahmed, mataimakin dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar Labour (LP), ya bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima su yi murabus.
Baba-Ahmed yace a bar shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio ya sake gudanar da zaben shugaban kasa bayan Tinubu da Shettima sun yi murabus.
Ya yi wannan kiran ne a wata hira da aka yi da shi a gidan Talabijin na Arise yayin da yake amsa tambaya kan yiwuwar yin aiki da gwamnatin Tinubu.
Baba-Ahmed ya tabbatar da cewa an yi wa Tinubu da Shettima rantsuwa da yaudara bayan zaben shugaban kasa na 2023. Don haka, LP ba zai hada kai da abin da ya dauka a matsayin haramtacciyar gwamnati ba.
A kalaman sa, âShin Tinubu da Shettima za su iya yin murabus kawai su bar Shugaban Majalisar Dattawa ya sake gudanar da wani zabe? An yi musu rantsuwa da zamba, kuma ba za mu yi aiki da gwamnatin shege ba. Idan ba tsarin mulki ba ne, ba mu taba shi ba.â
Jawabin nasa ya biyo bayan wani taron manema labarai da dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar LP, Peter Obi, inda ya zargi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da kotun koli da gazawa wajen tafiyar da alâamuran zabe.