Mai baiwa gwamna jihar LegasBabajide Sanwo-Olu shawara na musamman kan harkokin magudanun ruwa da albarkatun ruwa na jihar, Joe Igbokwe, ya ce, ya kamata a dauki dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar All Progressives Congress (APC) Bola Ahmed Tinubu a matsayin Kirista.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan cece-kucen da ake tafkawa dangane da zaben abokin takarar Asiwaju.
Ku tuna cewa Tinubu, tsohon gwamnan jihar Legas wanda musulmi ne, a ranar Lahadin da ta gabata ya bayyana wani tsohon gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima, wanda shi ne babban musulmi a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023.
Da yake mayar da martani Igbokwe wanda ya goyi bayan zabin Tinubu ya ce, matar Asiwaju, Oluremi Tinubu fasto ce a Cocin Redeemed Christian Church of God, RCCG.
Wani rubutu a shafinsa na Facebook ya ce, Tinubu da matarsa daya ne bisa koyarwar Littafi Mai Tsarki.
Ya rubuta, âShin, kun san cewa matar Asiwaju limami ce a Cocin Redeemed Christian Church of God? Ashe, mata da miji ba su Ĉara zama Éaya bisa ga Littafi Mai Tsarki baâ?