fidelitybank

Tinubu da Buhari kan su a hade ya ke har yanzu – Gwamnan Nasarawa

Date:

Gwamnan jihar Nasarawa da ke Najeriya, Abdullahi Sule ya ce wasu na son yin amfani da rashin “zuwan tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari Abuja” domin nuna cewa akwai ɓaraka tsakaninsa da shugaban ƙasar mai ci, Bola Tinubu.

Gwamna Sule ya bayyana haka ne yayin da alamu suka bayyana cewa an samu ɓaraka tsakanin makusantan tsohon shugaban ƙasar, waɗanda suka kasance a jam’iyyar CPC, wadda Buhari ya jagoranta kafin shiga haɗakar da ta samar da jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar.

A baya-bayan nan wani ɓari na ƴaƴan tsohuwar jam’iyyar ta CPC sun bayyana mubaya’arsu ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, sai dai kwanaki kaɗan bayan hakan wasu ƴaƴan tsohuwar jam’iyyar kuma waɗanda ke da matuƙar kusanci da Buhari sun nesanta kansu daga mubaya’ar.

Haka nan sauya sheƙar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, wanda shi ma makusancin tsohon shugaban ƙasar ne ya ƙara ɗora ayar tambaya kan alaƙar da ke tsakanin tsohon shugaba Muhammadu Buhari da kuma shugaba mai ci Bola Tinubu.

Sai dai a tattaunawarsa da BBC, Abdullahi Sule ya ce “maganar cewa abubuwa sun yi tsamari duk kuskure ne…don ba ya zuwa Abuja shi ne za a ce ba ya tare da wannan gwamnatin, ina jin wannan kuskure ne.”

Haka nan gwamnan ya musanta batun cewa sun ziyarci tsohon shugaban ƙasar da nufin shawo kansa kada ya fice daga jam’iyyar.

An riƙa zargin cewa wasu daga cikin gwamnonin sun kai ziyara wa tsohon shugaban ƙasar a ƙoƙarin tabbatar da goyon bayansa ga Tinubu, sai dai Sule ya: “mu dai ba mu yi maganar dannan ƙirji a wurin ba…ba a yi haka ba.”

Al’amura na ƙara zafi a siyasar Najeriya bayan kokawar da al’ummar ƙasar ke yi kan wahalhalu sanadiyyar matsin tattalin arziƙi bayan wasu manufofi na gwamnatin Shugaba Tinubu.

Wannan ya bai wa ƴan adawar siyasa damar sukar gwamnatin, inda ake ganin alamun suna ƙoƙarin yin haɗaka domin ƙalubalantarsa a babban zaɓen ƙasar na gaba da za a gudanar a shekarar 2027.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp