fidelitybank

Tinubu da Buhari kan su a hade ya ke har yanzu – Gwamnan Nasarawa

Date:

Gwamnan jihar Nasarawa da ke Najeriya, Abdullahi Sule ya ce wasu na son yin amfani da rashin “zuwan tsohon shugaban ƙasar, Muhammadu Buhari Abuja” domin nuna cewa akwai ɓaraka tsakaninsa da shugaban ƙasar mai ci, Bola Tinubu.

Gwamna Sule ya bayyana haka ne yayin da alamu suka bayyana cewa an samu ɓaraka tsakanin makusantan tsohon shugaban ƙasar, waɗanda suka kasance a jam’iyyar CPC, wadda Buhari ya jagoranta kafin shiga haɗakar da ta samar da jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar.

A baya-bayan nan wani ɓari na ƴaƴan tsohuwar jam’iyyar ta CPC sun bayyana mubaya’arsu ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, sai dai kwanaki kaɗan bayan hakan wasu ƴaƴan tsohuwar jam’iyyar kuma waɗanda ke da matuƙar kusanci da Buhari sun nesanta kansu daga mubaya’ar.

Haka nan sauya sheƙar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, wanda shi ma makusancin tsohon shugaban ƙasar ne ya ƙara ɗora ayar tambaya kan alaƙar da ke tsakanin tsohon shugaba Muhammadu Buhari da kuma shugaba mai ci Bola Tinubu.

Sai dai a tattaunawarsa da BBC, Abdullahi Sule ya ce “maganar cewa abubuwa sun yi tsamari duk kuskure ne…don ba ya zuwa Abuja shi ne za a ce ba ya tare da wannan gwamnatin, ina jin wannan kuskure ne.”

Haka nan gwamnan ya musanta batun cewa sun ziyarci tsohon shugaban ƙasar da nufin shawo kansa kada ya fice daga jam’iyyar.

An riƙa zargin cewa wasu daga cikin gwamnonin sun kai ziyara wa tsohon shugaban ƙasar a ƙoƙarin tabbatar da goyon bayansa ga Tinubu, sai dai Sule ya: “mu dai ba mu yi maganar dannan ƙirji a wurin ba…ba a yi haka ba.”

Al’amura na ƙara zafi a siyasar Najeriya bayan kokawar da al’ummar ƙasar ke yi kan wahalhalu sanadiyyar matsin tattalin arziƙi bayan wasu manufofi na gwamnatin Shugaba Tinubu.

Wannan ya bai wa ƴan adawar siyasa damar sukar gwamnatin, inda ake ganin alamun suna ƙoƙarin yin haɗaka domin ƙalubalantarsa a babban zaɓen ƙasar na gaba da za a gudanar a shekarar 2027.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp