Sanata Adams Oshiomhole, dan majalisa mai wakiltar mazabar Edo ta Arewa, ya ce shugaban kasa Bola Tinubu bai yi alkawarin magance dimbin kalubalen da ke fuskantar al’ummar kasar cikin dare daya ba.
Tsohon gwamnan jihar Edo, wanda ya yi magana a ranar Lahadin da ta gabata yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels, ya ce shugaban kasa ba matsafi bane.
A cewarsa, jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulkin kasar, har yanzu tana kan turbar alkawuran da ta dauka a yakin neman zabe, inda ta ce babu wani lokaci da ta yi alkawarin magance matsalolin Najeriya na tsawon sa’o’i 24.
Dan majalisar ya bayyana fatansa na ganin gwamnatin Tinubu za ta cika alkawuran da ta dauka, yana mai jaddada cewa shugaban kasar ya yi ta bakinsa a kwanakin baya.