fidelitybank

Tinubu bai halarci taron da Buhari ke jagoranta ba na APC

Date:

A halin yanzu dai shugaban kasa Muhammadu Buhari yana karbar bakuncin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, karkashin jagorancin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar, Kashim Shettima, a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Sai dai dan takarar shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, bai halarci taron ba.

Wadanda suka halarci taron akwai shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan; Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu; Shugaban kungiyar gwamnonin ci gaba kuma gwamnan jihar Kebbi, Atiku Bagudu; Gwamnonin Borno, Yobe, Nasarawa, Gombe — Babagana Zulum, Mai Mala Buni, Abdullahi Sule da Yahaya Inuwa, bi da bi.

Haka kuma akwai mataimakin shugaban jam’iyyar APC na kasa ta Kudu, Emma Enuku; Mataimakin kakakin majalisar wakilai, Idris Wada; tsohon kakakin majalisar wakilai, Dimeji Bankole, da dai sauransu.

Taron masu ruwa da tsaki na zuwa ne kwanaki biyu bayan bayyana Shettima a matsayin babban abokin takarar Tinubu.

Tsohon gwamnan jihar Borno, wanda ya je Villa don ganin Buhari a ranar Laraba, ya shaida wa manema labarai cewa “ya ji dadi” don gode wa shugaban da kansa, kafin ya dawo tare da wata babbar tawaga ranar Juma’a.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp