fidelitybank

Tinubu bai ce gwamnan banki ya yi murabus ba – Fadar Shugaban Ƙasa

Date:

Fadar shugaban kasa ta ce, shugaban kasa Bola Tinubu, bai nemi Yemi Cardoso ya yi murabus daga mukaminsa na gwamnan babban bankin Najeriya CBN ba.

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, inda ya karyata rahotannin da ke cewa Tinubu ya ba da umarnin murabus din Cardoso.

A cikin sakon da ya fitar ta hannun jami’insa na X ranar Talata, kakakin shugaban ya bayyana rahoton a matsayin tarin karya.

“Duk karya ne. Shugaba Tinubu bai nemi Yemi Cardoso ya yi murabus ba,” in ji Onanuga.

Rahoton ya bayyana cewa, shugaba Tinubu ya bayar da umarnin ne ga Cardoso kafin ya tashi zuwa kasar Sin, duk da kokarin da shugabannin Yarbawa masu fada a ji na ganin ya ci gaba da rike shi.

Ku tuna cewa Gwamnan CBN ya sha suka kan gazawar sa wajen magance kalubalen tattalin arzikin da ake fama da shi da kuma daidaita darajar Naira.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp