fidelitybank

Tinubu ba zai taba goyon baya a wawure dukiyar al’umma ba – Adeleke

Date:

Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya tabbatar da cewa shugaban kasa Bola Tinubu ba zai taba goyon bayan a wawure dukiyar al’umma ba.

Ya yi magana ne a matsayin martani ga zargin da jam’iyyar APC ta Osun ta yi game da wata farar takarda da aka fitar kwanan nan.

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar sun yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da jami’an tsaro da su taimaka wajen ceto jihar daga mulkin kama karya na Gwamna Adeleke da jam’iyyarsa ta PDP mai mulki.

Gwamnatin jihar Osun a ranar 18 ga watan Junairu, 2024, ta fitar da wata farar takarda akan sarakunan gargajiya da kuma karbo kadarorin al’umma da ake zargin wasu masu rike da mukamai na siyasa a karkashin gwamnatin Adegboyega Oyetola.

A cewar Gwamna Adeleke a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Olawale Rasheed ya fitar, “Shugaban kasa a kodayaushe ya yaba masa kan yadda ya kawar da duk wata matsala da ya hadu da shi a Osun, yayin da ya kuma jaddada cewa shugaba Tinubu ya kyamaci sace dukiyar al’umma.

“Na sha yin mu’amala da Shugaba Tinubu, kuma na san ya yaba da kokarin da na yi wajen tsaftace dimbin matsalolin da na fuskanta a Osun.

“Daga ayyukan shugaban kasa, ya nuna cewa shi mutum ne mai bin ka’ida, don haka ba zai taba goyon bayan wawure dukiyar jama’a ba. Yanzu abin takaici ne yadda Osun APC ke nuna ayyukan da suka saba wa salon mulkin Shugaban kasa

“Moreso, a farkon gwamnatinmu, na kafa kwamitin kwato kadarori, tare da sanar da mafi yawan wadanda ke da kadarorin gwamnati kan bukatar dawo da su.

“Yanzu shi ne rahoton kwamitin da nake aiki da shi kamar yadda mutanen kirki na jihar suka bukata.”

Gwamna Adeleke, yayin da yake tabbatar da cewa ya na mulkin jihar ne ba tare da bangaranci ba, ya bayyana cewa bai jawo wani abokin adawar siyasa ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa ba ko da akwai wasu dalilai na yin hakan.

A yayin da yake kira ga wadanda aka nada a gwamnatin da ta gabata a jihar da su mayar da dukkan kadarorin gwamnati da ke hannunsu, Adeleke ya yi gargadin cewa gwamnatinsa ba za ta bari a kwato duk kadarorin gwamnati da aka wawashe ba.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp