Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El Rufa’i ya ce ya faɗa wa shugaba Bola Tinubu cewa ba ya son wani muƙami a gwamnatinsa.
El Rufa’i ya bayyana haka ne a shafinsa na X yayin martani ga babban mai taimaka wa shugaban ƙasa kan sadarwar tsare-tsaren gwamnati, Daniel Bwala, wanda ya ce El Rufa’i ya ji tsoron Allah bayan da ya fito fili ya caccaki jam’iyyar APC da kuma kiran ta mai mulkin da ta “sauka daga aƙidun dimkoraɗiyya da aka kafa ta a kai”.
“Na faɗa wa Tinubu ƙarara cewa ba na buƙatar kowane irin muƙami a gwamnatinsa,” in ji El Rufa’i.
Ya ce yana mamakin irin yadda Daniel Bwala da takwarorinsa da suka koma jam’iyyar APC a baya-bayan nan ke ta yayata batun cewa an hana shi muƙami, abin da ya ce ba ya so tun da farko.
“Ina mayar maka da martani ne saboda ina tunanin cewa kai mai fahimta ne wanda ke neman aiki, ba irin wasu mutane ba.
“Ku mutane ne da ke karɓar albashi kowane wata don ku fara fitowa a shafukan sada zumunta wajen kare kowane irin abu da gwamnatin Asiwaju ta yi ko kuma ta ƙasa yi,” in ji tsohon gwamnan na Kaduna.
Ya ce ko da ace yana cikin gwamnatin shugaba Tinubu – babu abin da zai hana shi furta kalaman da ya yi kan abin da ke faruwa a jam’iyyar da ya ce su suka kirkiro – har ma da kawo gwamnati mai ci.