fidelitybank

Tinubu ba na bukatar mukami a gwamnatin ka – El-Rufa’i

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El Rufa’i ya ce ya faɗa wa shugaba Bola Tinubu cewa ba ya son wani muƙami a gwamnatinsa.

El Rufa’i ya bayyana haka ne a shafinsa na X yayin martani ga babban mai taimaka wa shugaban ƙasa kan sadarwar tsare-tsaren gwamnati, Daniel Bwala, wanda ya ce El Rufa’i ya ji tsoron Allah bayan da ya fito fili ya caccaki jam’iyyar APC da kuma kiran ta mai mulkin da ta “sauka daga aƙidun dimkoraɗiyya da aka kafa ta a kai”.

“Na faɗa wa Tinubu ƙarara cewa ba na buƙatar kowane irin muƙami a gwamnatinsa,” in ji El Rufa’i.

Ya ce yana mamakin irin yadda Daniel Bwala da takwarorinsa da suka koma jam’iyyar APC a baya-bayan nan ke ta yayata batun cewa an hana shi muƙami, abin da ya ce ba ya so tun da farko.

“Ina mayar maka da martani ne saboda ina tunanin cewa kai mai fahimta ne wanda ke neman aiki, ba irin wasu mutane ba.

“Ku mutane ne da ke karɓar albashi kowane wata don ku fara fitowa a shafukan sada zumunta wajen kare kowane irin abu da gwamnatin Asiwaju ta yi ko kuma ta ƙasa yi,” in ji tsohon gwamnan na Kaduna.

Ya ce ko da ace yana cikin gwamnatin shugaba Tinubu – babu abin da zai hana shi furta kalaman da ya yi kan abin da ke faruwa a jam’iyyar da ya ce su suka kirkiro – har ma da kawo gwamnati mai ci.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp